Home Blog Page 2

Tinubu ya bayar da albashinsa gaba ɗaya ga sojojin Najeriya

0

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da kafa wani asusu na musamman domin tallafa wa jami’an rundunar sojin Najeriya.

Yayin bikin cika shekaru 74 da haihuwarsa, Tinubu ya ce cikin waɗanda za su amfana har da waɗanda suka jikkata da kuma iyalan waɗanda suka rasu a bakin aiki.

A wata sanarwa da ya fitar, shugaban ya ce ya umarci babban akanta na ƙasa da ya buɗe wani asusu na musamman domin wannan shiri.

Tinubu ya kuma bayyana cewa zai bayar da dukkan albashinsa tun daga lokacin da ya hau mulki a matsayin tallafin farko ga asusun.

Ya ce, “A matsayin ƙuduri na kaina, zan zuba duk albashina tun daga lokacin da na karɓi mulki cikin wannan asusu domin fara shi.”

Shugaban ya yi kira ga gwamnoni, yan majalisar dokoki, yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki da su mara wa wannan shiri baya.

Ya jaddada muhimmancin girmama sadaukarwar jami’an tsaro, yana mai cewa wajibi ne a kula da su da iyalansu, ba sadaka ba ce illa hakki ne na ƙasa.

‘Yan Majalisa 27 Sun Fice Daga PDP da Wasu Jam’iyyu Zuwa APC, ADC da Sauransu

0

An samu yawaitar masu sauya sheƙa a Majalisar Wakilai ta Tarayya, inda jam’iyyun ADC, APC da wasu suka samu ƙarin mambobi, yayin da ‘yan siyasa ke ƙara sauya matsayi gabanin zaɓen 2027.

Rahotanni sun nuna cewa Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya karanta sanarwar sauya sheƙar a zaman majalisa na ranar Talata.

Jimillar ‘yan majalisa 27 ne suka sauya sheƙa a wannan karo, wanda ake ganin yana daga cikin manyan sauye-sauyen siyasa a majalisar, ƙasa da shekara guda kafin ‘yan Najeriya su sake zuwa rumfunan zaɓe domin zaɓar shugabanninsu.

Daga cikin waɗanda suka sauya sheƙar, mutum 14 sun koma jam’iyyar APC.

Sannan mutum 8 sun koma jam’iyyar ADC, waɗanda suka haɗa da ‘yan majalisa 5 daga PDP, 2 daga LP, da kuma 1 daga APC. A gefe guda kuma, jam’iyyar APP ta samu ‘yan majalisa 2, ɗaya daga PDP da ɗaya daga LP.

Haka zalika jam’iyyar Accord Party ta samu sababbin ‘yan majalisa 2 daga PDP, wanda hakan ya ƙara ƙarfin jam’iyyar, wacce ke mulki a jihar Osun.

‘Yan majalisar sun bayyana cewa sun sauya sheƙa ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyunsu na baya.

Wasu daga cikin ‘yan majalisar da suka sauya sheƙa sun haɗa da:

Aliyu Madaki – daga NNPP zuwa APC (Dala, Kano)

Tijjani Abdulkadir Jobe – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Ghali Tijjani Mustapha – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Shehu Bello – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Dankawu Idris – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Hussain Hassan Shehu – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Rabiu Yusuf – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Garba Mohammed Chiroma – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Ibrahim Mohammed – daga NNPP zuwa APC (Kano)

Sauran sun haɗa da: Jaafaru Yakubu – daga PDP zuwa APC (Taraba)

Sadiq Abbas Tafida – daga PDP zuwa APC (Taraba)

Bello Shinkafi – daga PDP zuwa APC (Zamfara)

Yaya Bauchi Tongo – daga PDP zuwa ADC (Gombe)

Umar Yusuf Yabo – daga PDP zuwa ADC (Sokoto)

Haka kuma akwai wasu da suka koma jam’iyyun APP da Accord daga PDP da LP a jihohin Imo da Osun.

Masu sharhi na ganin cewa wannan sauya sheƙa na nuna yadda siyasar Najeriya ke shiga sabon yanayi na sake fasali, yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

Kotu ta yankewa wasu ‘yan fashi hudu daurin shekaru 10 a gidan yari

0

Babbar kotun tarayya a Kano karkashin Mai shari’a Adam Abdullahi ta yankewa wasu mutane hudu hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari tare da tarar naira 10,000 kowannensu, bayan samun su da laifin fashi da makami.

Mutanen da aka yankewa hukuncin sun hada da Shafi’u Abubakar, Usman Suleiman, Usman Sa’idu da Ali Isa, wadanda mazauna unguwar Rijiyar Lemo ne a Kano.

An gurfanar da su ne bisa tuhume-tuhume uku da suka hada da hada baki domin aikata laifi da kuma fashi da makami, laifukan da suka saba doka karkashin sashe na 97 da 298(c) na kundin Penal Code.

A ranar 22 ga watan Yuli 2024, tsakanin karfe 3:00 zuwa 4:00 na dare, masu laifin sun shiga wasu gidaje dauke da muggan makamai a unguwannin Bankaura da Sabon Garin Doka da ke karamar hukumar Ungogo.

A cewar takardar tuhumar farko, masu laifin sun kai hari gidajen,Malam Abdullahi Musa da Mansur Mu’azu, tare da kwace musu kayayyaki masu daraja.

A tuhuma ta biyu, kotu ta tabbatar da cewa sun sace wayoyi guda biyu, babur kirar Lifan mai darajar naira 700,000 da kuma kudi daga hannun Abdullahi Musa.

Sai kuma a tuhuma ta uku, an ce sun kwace kudin naira 201,000 da kuma kudin CFA 500 daga hannun Mansur Mu’azu a gidansa da ke Sabon Garin Doka.

Lauyan gwamnati, Barrista Ibrahim Garba Arif, ya gabatar da shaidu guda biyu domin tabbatar da zargin.

Sai dai lauyan wadanda ake kara, Barrista Basira Yunus, ta bayyana cewa wadanda ake tuhumar sun sauya matsayinsu inda suka amince da zargin da ake musu.

Bayan nazarin shari’ar, kotun ta same su da laifi a dukkan tuhume-tuhumen, tare da yanke musu hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari da kuma biyan tarar naira 10,000 kowannensu kan kowane laifi.

Kotun ta kuma umarci cewa za a gudanar da hukuncin ne a lokaci guda (concurrently), daga ranar da aka kama su, wato 22 ga watan Yuli 2024.

“Tunda aka hana Kano cigaba, to Kano za ta mayar da martani a akwatin zabe wannan shi yafi komai sauki” Salihu Tanko Yakasai

0

Aminu Abdullahi Ibrahim

Tsohon dan takarar gwamnan Kano a jam’iya PRP ya ce Shugaba Bola Tinubu na tunanin zai iya mayar da Kano jiha mai jam’iyya daya, ba ta hanyar ayyukan cigaba da inganta rayuwar al’umma ba, sai ta hanyar dabarun siyasa” Salihu Tanko Yakasai

Ya bayyana haka ne cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Laraba.

Ya ce wannan fahimta ta shugaban kasa kuskure ce akan siyasar Kano.

Ya kara da cewa tun daga zamanin NEPU har zuwa lokacin Santsi da Tabo, Kano ba ta taba zama jiha mai jam’iyya daya ba, kuma ba za ta taba zama haka ba.

A cewarsa jihar Kano ba Lagos ba ce.

Ya kara da cewa Kano jiha ce ta siyasar kishin al’umma da tsayawa kan gaskiya, da tarbiyar da Mallam Aminu Kano.

Ya ce suna adawa ne domin neman ci gaban kasa da al’umma, ingantaccen shugabanci, adalci da rikon amana.

Salihu Tanko Yakasai ya ce aka yi wa Kano da zai sa Tinubu yayi tunanin kowa sai ya goyi bayan sa.

Yayi zargin cewa an mayar da hankali kan ayyuka a Lagos da karkatar da nade-nade ga yarbawa kadai yayin da aka yi watsi da korafe-korafen alummar Kano.

A cewarsa biyayya ga shugabanci na samuwa ne ta hanyar adalci da kyautatawa, ba a tilasta shi ta dabarun siyasa da wayo ko cin amana ba.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya ne Salihu Tanko Yakasai ya sanar da komawarsa jam’iyar ADC.

Majalisar Dattawa ta amince da bukatar shugaba Tinubu ta ciyo bashin dala biliyan 6

0

Majalisar Dattawa ta amince da bukatar bashin dala biliyan 6 da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gabatar domin gudanar da ayyukan more rayuwa, biyan basussuka da kuma gyaran tashoshin jiragen ruwa.

Amincewar ta biyo bayan nazarin wasiƙu biyu da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta a zaman majalisar.

A wasiƙa ta farko, Shugaba Tinubu ya nemi amincewa da bashin dala biliyan 5 daga bankin First Abu Dhabi Bank da ke Hadaddiyar Daular Larabawa.

Ya bayyana cewa idan aka karɓi bashin gaba ɗaya, zai ƙara yawan bashin Najeriya daga dala biliyan 110.3 zuwa dala biliyan 115.3.

Ya kuma bukaci a yi amincewar cikin gaggawa, yana mai cewa za a tabbatar da bashin da takardun kudi na Naira.

A wasiƙa ta biyu, Shugaban ya nemi amincewar bashin dala biliyan 1 domin gyaran tashoshin ruwa na Lagos Port Complex da Tin Can Island Port.

An bayyana cewa bankin Citibank London ne ke shirya bashin, tare da goyon bayan UK Export Finance.

A cewar Tinubu, kudaden za su taimaka wajen zamanantar tashoshin jiragen ruwa, inganta ayyukansu, ƙara tsaro da kuma daidaita su da ƙa’idojin duniya.

Ya ƙara da cewa gyaran zai magance matsalolin da suka dade suna addabar tashoshin tare da ƙarfafa tattalin arziki ta hanyar bunƙasa harkokin kasuwanci da sufuri.

Shugaban ya kuma bayyana cewa bashin zai ɗauki shekaru 14 kafin a biya, ciki har da wa’adin shekaru huɗu na fara amfani da shi, tare da ƙarin kuɗaɗen kaso 1.1 cikin ɗari na karuwa da kuma kaso 1.07 cikin ɗari na kuɗin inshora na UKEF.

Tun da farko, shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan basussuka na cikin gida da na waje, Sanata Aliyu Wamakko, ya ce kwamitin ya yi cikakken nazari kan bukatun kafin gabatar da rahotonsa ga majalisar domin amincewa.

Ɗan tsohon mataimakin shugaban Kasa Atiku Abubakar ya ajiye muƙaminsa a gwamnatin Adamawa

0

Adamu Atiku Abubakar, ɗan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi murabus daga muƙaminsa na Kwamishinan Ayyuka da Makamashi na Jihar Adamawa.

A cikin wasiƙar murabus ɗinsa mai kwanan wata 2 ga Maris, 2026, wadda ya aika wa Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, Adamu ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan “zurfin tunani da yin nazari.”

Adamu ya bayyana cewa kasancewarsa a muƙamin wata babbar dama ce da ya ɗauka a matsayin karramawa. Ya gode wa gwamnan bisa ba shi damar yin aiki a ƙarƙashin jagorancinsa tare da bayar da gudunmawa wajen bunƙasa jihar.

Haka kuma, ya gode wa al’ummar Jihar Adamawa bisa goyon baya da amincewar da suka nuna masa a tsawon lokacin da yake kan muƙami. Ya ce yanayin aiki mai kyau da gwamnan ya samar ya ba shi damar gudanar da aikinsa cikin ƙwazo da jajircewa.

A ƙarshe, ya yi addu’ar Allah Ya ba gwamnan ƙarfi da shiriya domin ci gaba da yi wa jihar hidima.

Rahotanni sun nuna cewa Adamu bai sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC ba. Kuma an lura cewa bai halarci taron kwamishinoni 22 da suka raka Gwamna Fintiri domin sanar da ficewarsu daga jam’iyyar PDP zuwa APC a ranar 27 ga Fabrairu, 2026 ba.

ICPC ta sanar da kwato na’urar satar bayanai ta wayar tarho a gidan El-Rufai da ke Abuja

0

Hukumar yaki da cin hanci ta (ICPC) ta sanar da kwato wasu kayan aiki da ake zargin za a iya amfani dashi wajen sauraron tattaunawar wayar tarho a gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir el-Rufaida ke Abuja.

Hukumar ta ce ta samu umarnin Kotun Majistare da ke Bwari a Babban Birnin Tarayya (FCT) domin tsare el-Rufai na tsawon kwanaki 14, wanda wa’adinsa zai ƙare a ranar Alhamis.

Haka kuma, hukumar ta roƙi Babbar Kotun Bwari dake Abuja da ta yi watsi da ƙarar da el-Rufai ya shigar, wadda ke zargin tauye masa ’yancinsa na ɗan Adam.

ICPC ta ce tsohon gwamnan na da zarge-zargen cin hanci da rashawa da ya kamata ya amsa, ciki har da tambayoyi kan inda Yuro miliyan daya da dubu 400 suka shiga; da kuma tura wasu kuɗi zuwa asusun da ba a bayyana ba har N428,122,180.18, da sauransu.

Hukumar ta kuma tabbatar da cewa wani mataimaki na tsohon gwamnan, wanda ake zargin yana da alaƙa da lamarin, ya fice daga ƙasar.

Hukumar ta ce dukkan kayan da ake zargi, an kwato su ne a gaban matar tsohon gwamnan, Hadiza Isma el-Rufai, da ɗansa, Hon. Bello el-Rufai.

ICPC ta kuma zargi tsohon gwamnan da ƙin ba da haɗin kai ga masu bincike, inda ta ce ya zaɓi yin shiru har sai an kai shi gaban kotu. Ta ƙara da cewa wani mataimaki da ke da alaƙa da binciken ya tsere daga ƙasar.

Hukumar tsaro ta DSS ta murƙushe kungiyar safarar makamai a Gombe, Ta kwato rokoki

0

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta sanar  cewa jami’anta sun murƙushe wata ƙungiyar da ake zargi da safarar makamai a Jihar Gombe, tare da kama mutane biyu da ake zargi, da kuma kwato makamai masu haɗari ciki har da rokoki na RPG.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa an cafke Muhammed Alhaji Mohammed mai shekaru 55 da Sani Gesha mai shekaru 47 a Mararaban Tula da ke Ƙaramar Hukumar Kaltungo, yayin da suke tafiya cikin wata mota kirar Toyota Corolla mai launin toka, mai lambar Taraba JAL475YQ.

Kayayyakin da aka kwato sun haɗa da kananan rokoki biyu na RPG, na’urar harba rokoki da sauran makamai.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa kamen ya biyo bayan makonni uku na sa ido a ɓoye kan wata babbar hanyar safarar makamai a jihohin Bauchi, Gombe, Taraba da Adamawa.

Rahotanni sun nuna cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu a yayin tambayoyi, inda suka ce makaman za a kai su ne zuwa wani mutum a ƙauyen Kukawa da ke Ƙaramar Hukumar Alkaleri a Jihar Bauchi.

A wani cigaban mai alaƙa da wannan, jami’an DSS sun kuma ceto wani yaro ɗan shekara shida mai suna Mohammed Jabir, wanda ake zargin an yaudare shi tare da sace shi da sunan koya masa babur.

An kama wanda ake zargi, Salisu Hussain, dangane da lamarin, yayin da aka miƙa yaron ga iyayensa cikin farin ciki.

Hukumar ta ce duk waɗanda ake zargi suna hannunta, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.