Zargin ɓatancin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakanin Tinubu da jam’iyyun PDP da LP

Zargin ɓata suna da ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kan abokan hamayyarsa na PDP da LP na cigaba da haifar da ce-ku-ce-ce tsakanin magoya bayan jam’iyyun.

Wannan batu ya fito fili ne lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya ce zai shigar da karar wasu kafofin yaɗa labarai da kuma jam’iyyun da ya zarga na yaɗa labaran karya domin ɓata masa suna da takararsa.

A karshen makon jiya ne aka rinƙa yawo da wata sanarwa da sunan hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, da ke cewa za ta binciki labaran da ke fitowa daga Amurka kan Bola Tinubu, da ke alaƙanta shi da harkar migayun kwayoyi.

Sai dai daga baya INEC ta fitar da sanarwa ta shafukanta na sada zumunta tana nesanta kanta da wannan sanarwa.

Lamarin ya harzuka jam’iyyar APC da tursasa mata fitar da sanarwa inda ta zargi PDP da LP da shirya mata manaƙisa.

Leave a Reply