Aƙalla mutum shida sun mutu a wani harin ‘yan bindiga a kudu maso gabashin jihar Anambran Najeriya.
An kai harin ne kan ayarin masu gangamin yaƙin neman zaben ranar 6 ga watan Nuwamba da ke tafe.
Mutane sun rasa rayukansu a musayar wuta tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga, sannan akwai da dama da suka jikkata a ɓarin-wutar da aka shafe sama da sa’a biyu a wata karamar hukuma.
Gwamna Willie Obiano na cikin mutanen da harin ya ritsa da su.
A watan da ya gabata ‘yan sanda suka rawaito cewa za su tura helikwafta shida domin taimakawa jami’an tsaro gabannin zaben da ke tafe a wata mai zuwa.