Ina Nan A Abuja, Ban Tafi Amurka Ba – Tinubu

Kwamitin ya bayyana hakan ne domin karyata rade-radin da ake yi cewa Tinubu ya keta hazo zuwa Amurka don ganawa da Shugaba Joe Biden.

Kakakin kwamitin, Bayo Onanuga ne ya bayyana wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) hakan ranar Laraba a Abuja.

Ya ce labarin Tinubu ya tafi Amurka ba gaskiya ba ne, don haka ya ce jama’a su yi watsi da shi.

Ya kara da cewa, hoton Tinubu tare da Shugaba Biden da aka yada sharrin mahassada ne kawai a fagen siyasa.

Leave a Reply