Hukumar tsaro ta DSS ta murƙushe kungiyar safarar makamai a Gombe, Ta kwato rokoki

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta sanar  cewa jami’anta sun murƙushe wata ƙungiyar da ake zargi da safarar makamai a Jihar Gombe, tare da kama mutane biyu da ake zargi, da kuma kwato makamai masu haɗari ciki har da rokoki na RPG.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa an cafke Muhammed Alhaji Mohammed mai shekaru 55 da Sani Gesha mai shekaru 47 a Mararaban Tula da ke Ƙaramar Hukumar Kaltungo, yayin da suke tafiya cikin wata mota kirar Toyota Corolla mai launin toka, mai lambar Taraba JAL475YQ.

Kayayyakin da aka kwato sun haɗa da kananan rokoki biyu na RPG, na’urar harba rokoki da sauran makamai.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa kamen ya biyo bayan makonni uku na sa ido a ɓoye kan wata babbar hanyar safarar makamai a jihohin Bauchi, Gombe, Taraba da Adamawa.

Rahotanni sun nuna cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu a yayin tambayoyi, inda suka ce makaman za a kai su ne zuwa wani mutum a ƙauyen Kukawa da ke Ƙaramar Hukumar Alkaleri a Jihar Bauchi.

A wani cigaban mai alaƙa da wannan, jami’an DSS sun kuma ceto wani yaro ɗan shekara shida mai suna Mohammed Jabir, wanda ake zargin an yaudare shi tare da sace shi da sunan koya masa babur.

An kama wanda ake zargi, Salisu Hussain, dangane da lamarin, yayin da aka miƙa yaron ga iyayensa cikin farin ciki.

Hukumar ta ce duk waɗanda ake zargi suna hannunta, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

Related Posts

ICPC ta sanar da kwato na’urar satar bayanai ta wayar tarho a gidan El-Rufai da ke Abuja

Hukumar yaki da cin hanci ta (ICPC) ta sanar da kwato wasu kayan aiki da ake zargin za a iya amfani dashi wajen sauraron tattaunawar wayar tarho a gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir…

Hello world!

Welcome to WordPress. This is your first post. Edit or delete it, then start writing!

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Ɗan tsohon mataimakin shugaban Kasa Atiku Abubakar ya ajiye muƙaminsa a gwamnatin Adamawa

Ɗan tsohon mataimakin shugaban Kasa Atiku Abubakar ya ajiye muƙaminsa a gwamnatin Adamawa

ICPC ta sanar da kwato na’urar satar bayanai ta wayar tarho a gidan El-Rufai da ke Abuja

ICPC ta sanar da kwato na’urar satar bayanai ta wayar tarho a gidan El-Rufai da ke Abuja

Hukumar tsaro ta DSS ta murƙushe kungiyar safarar makamai a Gombe, Ta kwato rokoki

Hukumar tsaro ta DSS ta murƙushe kungiyar safarar makamai a Gombe, Ta kwato rokoki

The Art of Crafting High-Quality Radio Content

The Art of Crafting High-Quality Radio Content

How We Keep Our Listeners Informed and Entertained

How We Keep Our Listeners Informed and Entertained

Exploring the Diverse Genres of Guarantee Radio FM

Exploring the Diverse Genres of Guarantee Radio FM