Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce a shirye yake ya sa hannu a aiwatar da hukuncin kisa a kan wanda ake zargi da kisan Hanifa muddin kotu ta yanke masa hukuncin.
Tuni dai wanda ake zargin mai suna Abdulmalik Tanko ya amsa aikata laifin da ake masa na sacewa tare da kisan dalibar mai shekara biyar.
Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, inda ya ce ba zai yi wata-wata ba wajen sanya hannu a zartar masa da hukuncin.