APC ta lashe kujerun sanata uku a Katsina amma Atiku ya doke Tinubu

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a jihar Katsina ta bayyana cewa jam’iyyar PDP ce ta lashe zaɓen shugaban ƙasa bayan samun ƙuri’u mafi rinjaye.

Sai dai a ɓangare guda jam’iyyar APC mai mulki ce ta lashe dukkanin kujerun majalisar dattijai, wato na yankin Daura, da Katsina ta tsakiya da kuma shiyyar Funtua.

A ɓangaren majalisar wakilan tarayya kuwa jam’iyyar PDP ce ta lashe kujeru tara daga cikin 15.

Leave a Reply