Wata babbar kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta yanke wa Mubarak Bala hukuncin shekara 24 a gidan yari kan laifin ɓatanci ga addinin Islama.
An yanke masa hukunci ne kan laifuka 18 da aka zarge shi ciki har da amsa laifin aikata saɓo da ya yi a gaban kotu.
Sai dai ya shaida wa kotun cewa lokacin da ya yi rubutu bai san cewar saƙon zai iya haifar da tashin hankali ba, sannan kuma hakan ya zama darasi a gare shi, nan gaba.
An kama Mubarak Bala, shugaban kungiyar waɗanda ba su yarda da addini ba ta Najeriya, a ranar 28 ga watan 2020 a gidansa da ke jihar Kaduna.
Sannan aka gurfanar da shi a gaban kotu a Kano bisa zargin aikata sabo ta hanyar wallafa wasu kalamai a shafinsa na Facebook.
Sakon da ya wallafa ya fusata al’ummar Musulmai a Najeriya.
Abin da ya faru a kotun
An fara ne da karanta wa Mubarak Bala tuhuma 14 da ake yi masa kan zargin saɓo.
Sai dai ya amsa aikata kusan laifi shida daga cikin tuhume-tuhumen da ake yi masa. Kana aka ci gaba da karanto masa laifukan nasa.
Ana karanta masa saƙonnin da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na Facebook da ya yi kalaman ɓatanci ga addinin Musulunci.
Ya amsa dukkan laifukansa kan dukkan tuhume-tuhume 14 da aka karanto masa da cewar ya aikata.
An bai wa lauyan Mubarak minti 15 saboda ya samu damar ganawa da wanda ake ƙara.
Bayan an koma zaman kotun ne sai lauyan ya sanar da kotu cewar wanda yake karewa zai sauya amsar da ya bai wa kotun.
Sai dai ana tsaka da tattaunawa ne sai Mubarak Bala ya sanar da kotu cewar ba zai sauya abin da ya faɗa da farko ba, saboda haka ya amsa laifukan da ake zarginsa da aikatawa.
Alkali ya tambaye shi ko ya san girman laifukan da ake zarginsa da yi da irin hukuncin da za a iya yanke masa? Sai Mubarak ya ce ya sani.
Ya ce babu wanda ya tursasa shi don ya amsa dukkan laifukan da ake zarginsa da aikatawa.
Sannan babu wanda ya yi masa alkawari, ko ya sanya masa wani ra’ayi, amma ya buƙaci kotu ta yi masa saussauci da kuma adalci.
Laifukan da ake zarginsa da aikatawa sun ci karo da sashe na 210 na kundun panel code.
Kotu ta same shi da laifin, sai dai ya ce a lokacin da ya yi rubutu bai san cewar zai rubutun ka iya tayar da hankali ba.
Ya ƙara da cewa hakan ya zama darasi a gare shi, nan gaba.
Hukuncin da aka yanke masa na nufin zai zauna a gidan yari na tsawon sherkara 24.