An samu ƙarin kashe-kashe a Najeriya cikin watan Nuwamba
Masana a ɓangaren tsaro sun buƙaci hukumomi a Najeriya su ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnatoci don inganta yaƙi da ayyukan ƴan bindiga masu addabar ƙasar.
Sun kuma buƙaci mahukunta su inganta tsarin tafiyar da lamurran tsaro ta yadda ba za a samu giɓin da zai ta’azzara matsalar ba.
Waɗannan shawarwarin na cikin rahoton da wani kamfanin tsaro mai suna Beacon Consulting ya fitar inda ya ƙiyasta cewa an samu ƙaruwar kashe-kashen mutane sanadin hare-haren da ƴan bindiga ke kai wa a sassan ƙasar cikin watan Nuwamban da ya wuce.
“An samu ƙari na yawan mace-mace da suka zarce kashi 50% daga watan Oktoba zuwa Nuwamban bana”.Dr Kabiru Adamu shi ne shugaban kamfanin kuma a cewarsa, talauci na ɗaya daga cikin abubuwan da ke ta’azzara matsalar tsaro a ƙasar.