Abin da zai faru idan Indiya ta zarta China yawan jama’a
Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta yi hasashen cewa Indiya za ta zarta China a matsayin ƙasar da ta fi yawan al’umma a duniya a tsakiyar watan Afrilu
Nan da tsakiyar watan Afrilu, an yi hasashen Indiya za ta zarta China a matsayin ƙasar da ta fi yawan al’umma a duniya.
Ƙasashen da ke nahiyar Asiya, tuni suke da yawan mutum fiye da biliyan 1.4, kuma a tsawon shekara 70 su ne ke da kashi ɗaya cikin uku na al’ummar duniya.
Ana sa ran nana da shekara sabuwar shekara al’ummar China za ta fara raguwa. A shekarar da ta gabata, an haifi yara miliyan 10.6, ɗan ƙari kaɗan yawan mutanen da suka mutu.
Su ma mazauna Indiya sun rage haihuwa sosai cikin tsawo shekaru – daga kashi 5.7 cikin 100 kan kowace mace ɗaya a 1950 zuwa haihuwar yara biyu.